Acts 22

1“Yanuwa da Ubanni, ku saurari kariya ta zuwa gare ku yanzu.” 2Da taron sun ji Bulus na magana a harshen Ibraniyawa sai sun yi tsit. Ya ce,

3Ni Bayahude ne daga garin Tarwasa na Kilikiya, amma a karkashin Gamaliyal aka ilimantar da ni. An horar da ni sosai bisa ga bin hanyar dokokin kakkaninmu. Ina da himma ga bin Allah kamar yadda ku ma kuna da ita. 4Na tsananta wa wannan Hanyan har ga mutuwa; na daure maza da mata sa’annan na jefa su cikin gidan yari. 5Hakannan ma babban firist da dukan dattawa za su ba da shaida cewa na karbi izini daga wurinsu domin ‘yan’uwa da ke a Dimashku, saboda in tafi can. Haki na shine in daure mabiyan Hanyan nan, in kawo su Urushalima domin a hukunta su.

6Sa’anda ina cikin tafiya, ina kuma kusa da Dimashku, da tsakar rana sai farat daya ga babban haske daga sama ya haskaka kewaye dani. 7Na fadi kasa sa’anan na ji murya na ce da ni, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani?’ 8Na amsa, ‘Wanene kai, Ubangiji?’ Ya ce mani, ‘Nine Yesu Banazarat wanda kake tsananta wa.’

9Wadanda ke tare da ni sun ga hasken, amma ba su gane muryar wanda ya yi magana da ni ba. 10Na ce, ‘Me zan yi ya Ubangiji?” Ubangiji ya ce mani, ‘Tashi ka tafi cikin Dimashku, a can za a fada maka abinda wajibi ne ka yi. 11Ban iya ganin wuri ba domin walkiyar hasken, sai na tafi cikin Dimashku ta wurin jagorancin wadanda ke tare da ni.

12A can na sami wani mai suna Ananiya, mai tsoron Allah bisa ga sharia, da kyakyawan suna kuma a gaban Yahudawa da ke zama a can. 13Ya zo gare ni ya ce, ‘Dan’uwa Shawulu, karbi ganin gari.’ A daidai wannan sa’a na gan shi.

14Sa’annan ya ce, ‘Allah na kakkaninmu ya zabe ka ka san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji muryar da ke fitowa daga bakinsa. 15Gama za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane game da abinda ka gani da wanda ka ji. 16A yanzu me ka ke jira? ‘Tashi a yi maka baftisma a wanke zunubanka, kana kira bisa sunansa.’

17Bayan da na dawo Urushalima, sa’anda ina addu’a a cikin haikali, sai na karbi wahayi. 18Na gan shi ya ce mani, ‘Gaggauta ka bar Urushalima yanzu, domin ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’

19Na ce, ‘Ubangiji, su da kansu sun san yadda na sa su a kurkuku na kuma doddoke wadanda suka gaskanta da kai a kowacce masujada. 20A sa’anda a ke zubar da jinin mashaidinka Istifanus, ina nan tsaye ina goyon baya, ina kuma lura da rigunan wadanda suka kashe shi.’ 21Amma ya ce mani, ‘Tafi, domin zan aike ka can wurin Al‘ummai.’

22Mutanen sun bar shi yayi magana har zuwa ga wannan lokacin. Amma sai suka ta da murya suna cewa, ‘A kawar da wannan dan taliki daga duniya: don bai kamata ya rayu ba.’ 23Sa’anda suke tadda muryarsu, suna jefar da tufafinsu da kuma baza kura a iska, 24babban hafsan ya umarta a kawo Bulus a farfajiyan. Ya umarta da cewa a bincike shi da bulala, domin ya san dalilin da suka ta da ihu gaba da shi haka.

25Bayan da suka daure shi da tsirkiya, Bulus ya ce wa Jarumin da ke kusa da shi, “Ko daidai ne bisa ga doka a yi wa Barome wanda ma sharia ba ta kashe shi ba bulala?” 26Da Jarumin ya ji haka, ya tafi wurin babban hafsan, yana cewa, “Me kake so ka yi? Gama wanan mutumin dan asalin Roma ne.”

27Babban hafsa ya zo ya ce masa, “Gaya mani, kai dan asalin Roma ne?” Bulus ya ce, “Haka ne.” 28Babban hafsan ya amsa masa, “Da kudi masu yawa na sayi yancin zama dan kasa.” Amma Bulus ya ce, “An haife ni dan kasar Roma. 29“Sai mutanen da sun zo su tuhume shi sun bar shi nan da nan. Babban hafsa shi ma ya tsorata da ya gane Bulus dan asalin Roma ne, domin ya riga ya daure shi.

Washegari, babban hafsan ya so ya san gaskiyar tuhuma da Yahudawa suke yi a kan Bulus. Sai ya kwance shi daga sarka, ya kuma umarci babban firist da dukan majalisa su sadu. Sai ya kawo Bulus ya sa shi a tsakiyarsu.

30

Copyright information for HauULB